Mid Term Break


Assalamu Alaikum Warahmatullahi wa barkatuh.
Zuwa ga iyaye masu daraja. 

HUTUN TSAKIYAR ZANGO (MID-TERM BREAK) 
Bayan gaisuwa irin ta addinin musulunci tare da fatan alheri, kasancewa zango na biyu na wannan shekara yazo tsakiya, kamar yadda aka sani akan bada hutu na tsakiyar zango. Hukumar makaranta tana sanarda iyaye cewa daga gobe Alhamis 25/02/2021 za’a tafi hutu wanda za’a dawo ranar Litinin 01/03/2021, hutun ya hada dukkan bangarorin biyu na safe da yamma.
 2. Bayan kokari da iyaye suke yi na ganin sun kawo yaransu makaranta akan lokaci, su kara himma akan hakan. 
3. Ana kara tunatar da Iyayen da basu biya kudin makaranta ba cewa suyi kokari su biya daga nan zuwa Lahadi 28/02/2021 domin daliban da aka yiwa register ne kawai za su samu damar cigaba da karatu daga Litinin 01/03/2021. 
4. Muna maraba da dukkan wani korafi ko kuma shawarwarin da zasu taimakemu domin inganta makarantar. Daga karshe muna matukar godiya bisa ga hadin kai da kuke bamu. 






                                                                                                                                   Sign 
                                                                                                                            Management
class="separator" style="clear: both;">

0 Comments